Shin Iran ta amince da kwance ɗamarar ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai?

    • Marubuci, بخش مانیتورینگ
    • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, بی‌بی‌سی
  • An wallafa
  • Lokacin karatu: Minti 2

Ziyarar Esmail Qaani, kwamandan Rundunar Quds ta IRGC, da ya kai Baghdad ba tare da sanarwa ba, ta haifar da muhawara, inda ake ta hasashe game da makomar ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da Iran ke goyon baya a Iraqi.

Rahotanni sun nuna cewa ya gana da manyan jami'an Iraqi domin tattauna batun kwance damarar waɗannan ƙungiyoyi.

Wasu kafafen yaɗa labarai na Larabawa sun yi iƙirarin cewa Qaani ya isar da "saƙo mai hancin damo" ga ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yayin wannan ziyarar; saƙon da a gefe guda ke jaddada ci gaba da riƙe makamai, a ɗaya gefe kuma yake ƙarfafa guje wa duk wani rikici da gwamnatin Iraqi da jami'an tsaro.

A lokaci guda, wasu manazarta a Iraqi sun ce akwai alamun wata yarjejeniya tsakanin gwamnatin Iraqi da ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai domin miƙa makamai; yarjejeniyar da, a cewarsu, za ta yiwu ne kawai idan Tehran ta ba da "hasken."

Babban abin da ya fi jan hankali game da martanin da aka mayar kan ziyarar Ismail Qaani ba tare da sanarwa ba shi ne rahotannin tattaunawarsa da manyan jami'an Iraqi kan kwance ɗamarar ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai.

Wasu kafafen yaɗa labarai sun bayyana ziyarar a matsayin wani yunƙuri na "ceto na ƙarshe na Iran kafin a kwance ɗamarar ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai."

Gidan talabijin na Al-Arabiya Al-Hadath na Saudi Arabiya ya bayar da rahoton cewa, "Iran na ƙoƙarin sake tsara tasirinta da matsayinta a Iraki a cikin wani gasa mai tsanani da lokaci."

Al-Mashhad, mai hedkwata a Dubai, ya bayar da rahoton cewa "Qaani na ƙarfafa ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai na Iraki da su guji miƙa makamansu," matakin da kafar ta ce wani ɓangare ne na ƙoƙarin Iran na ci gaba da tasirinta da kuma rage asararta a Iraki.

Shafin yanar gizo na Arab21 mai alaƙa da Qatar shi ma ya yi tambayar ko "Iraki za ta kasance a bakin ƙofar yaƙin basasa idan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai suka ƙi miƙa makamansu?"

Saƙon Qaani mai hancin damo

Al-Arabiya ta bayar da rahoton cewa Qaani ya gargaɗi ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da su guji duk wani rikici kai tsaye da jami'an tsaron Iraq, amma a lokaci guda ya buƙace su da su ci gaba da riƙe makamansu.

A halin da ake ciki, Al-Mashhad ta ce, "saƙon sirrin Qaani a Baghdad shi ne kada su miƙa makamai, kuma kada su shiga rikici da gwamnati."

Jaridar Lebanon ta Al-Nahar ita ma ta bayar da rahoto, tana ambaton majiyoyi, cewa Qaani ya isar da "saƙo mai hancin damo" ga ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da Iran ke goyon baya: "su riƙe makamansu domin tunkarar abin da Tehran ke ganin barazana ce daga Amurka da wasu ƙasashen yankin, yayin da a lokaci guda suke guje wa duk wani rikici kai tsaye da jami'an tsaron Iraki."

Alamar da Iran ta nuna

Wasu rahotanni sun nuna cewa Mista Qaani ya bayyana kwance ɗamarar ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a matsayin "soka wa Iran wuƙa a baya."

Mai sharhi kan harkokin siyasa Haider Hamid ya shaida wa kafar Al-Ghad mai hedkwata a Alkahira, wadda Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ke mara wa baya, cewa ziyarar Qaani wani ɓangare ne na ƙoƙarin Iran na hana duk wani rikici tsakanin ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da ke da kusanci da Iran da jami'an tsaron Iraki.

Kafar Sky News Arabic mai hedkwata a Abu Dhabi ita ma ta tattauna makomar makaman ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai na Iraki a wani shiri.

A cikin shirin, mai sharhi kan siyasar Iraqi Ghanem al-Abid ya ce da alama waɗannan ƙungiyoyi sun cimma yarjejeniya da gwamnatin Iraqi, bisa yarjejeniyar za su miƙa makamansu "idan suka samu izini daga Iran."