Ɗaliban jami’ar ABU za su wakilci Najeriya a gasar jami’o’in duniya
Ɗaliban jami’ar Ahmadu Bello (ABU) za su wakilci Najeriya a gasar ƙirƙire-ƙirƙire ta jami’o’in duniya ta ENACTUS da za a gudanar a birnin Sao Paulo na ƙasar Brazil
Za a gudanar da gasar ne a watan Nuwamba, kuma sun samu wannan damar ne bayan da suka lashe gasar ta ƙasa da aka gudanar a Najeriya.
Tawagar ENACTUS ta jami’ar ta zama zakarar Najeriya a gasar ta shekarar 2026, wadda aka gudanar a Legas daga ranar 11 zuwa 15 ga watan Agusta.
Gasar ta haɗa ɗalibai daga jami’o’i da kwalejojin fasaha daban-daban na ƙasar.
Nasarar ta ABU ta samu ne sakamakon wani aiki da tawagar ta gabatar kan magance matsalolin da ke addabar noman tumatur, musamman ƙwari da suke lalata tsirrai kafin girbi da kuma asarar amfanin gona bayan girbi.
Mai ba da shawara ga tawagar, Farfesa M.K. Aliyu, ya ce nasarar ba ta rasa nasaba daga irin bincike, haɗin gwiwa da al’umma da kuma jajircewar ɗaliban.