Najeriya za ta kwaso ƙarin ƴan ƙasarta daga Afrika ta Kudu kan ƙyamar baƙi

Asalin hoton, Getty Images
Gwamnatin Najeriya na shirin kwaso wasu ƙarin ƴan ƙasarta 83 daga Afirka ta Kudu, yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan ƙaruwa da zanga-zangar ƙyamar a ƙasar.
Ana sa ran mutanen za su isa Legas ranar Laraba, inda wasu mutane masu zaman kansu suka ɗauki nauyin tikitin dawowarsu.
Dawowar tasu na zuwa ne a lokacin da ƙungiyoyin masu zanga-zanga ke ci gaba da neman a fitar da baƙin da ba su da takardun zama, har ma suka sanya ranar 30 ga Satumba a matsayin wa’adin da suke son su fice daga ƙasar.
Fiye da mutum 150 ne suka gudanar da zanga-zanga a Durban, suna kira ga ƙasashen yankin kudancin Afirka su magance matsalar ƙaura ba bisa ƙa’ida ba.
Gwamnatin Afirka ta Kudu ta ce sama da mutum 80,000 ne aka kora ko kuma suka koma ƙasashensu da kansu yayin da take tsaurara matakan kula da shige da fice.





















