Yarjejeniyar Amurka da Iran za ta fara aiki nan taken- Pakistan
Pakistan ta ce yarjejeniyar da ka iya zama matakin farko na kawo ƙarshen yaƙin da ake tsakanin Amurka da Iran, za ta fara aiki nan take.
Firaminista Shehbaz Sharif, ya ce Iran za ta buɗe mashigar Hormuz ba tare da ɓata lokaci ba, sannan kuma za a buɗe duk wasu tasoshin gaɓar ruwan Iran da Amurka ta rufe.
Shugaba Trump ya ce ya sanya hannu kan jadawalin.
Yarjejeniyar ta ƙunshi kawo ƙarshen faɗan da ake da ga kowanne ɓangare, sannan kuma a cewar Amurka Iran ta yi alƙawarin cewa ba za ta riƙa ƙera makaman nukiliya ba.
Kakakin majalisar dokokin Iran kuma babban mai shiga tsakani na Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya yi magana da kafar talbijin ta ƙasar a kan batun a daren jiya Laraba inda ya kare yarjejeniyar.