Jarirai 14 sun mutu a gobarar asibiti a Pakistan
Akalla jarirai 14 ne suka mutu bayan wata gobara ta tashi a sashen kula da jarirai na asibitin Pakistan Institute of Medical Sciences, PIMS, da ke Islamabad, babban asibitin gwamnati na Pakistan.
Gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Laraba a sashen kula da mata masu juna biyu da masu haihuwa na asibitin, inda jarirai 15 ke ciki a lokacin.
Daga cikinsu, guda ɗaya ne kawai aka samu damar ceto.
Ministan Lafiya, Mustafa Kamal, ya ce gobarar ta samo asali ne daga wata matsala da ta faru a na'urar sanyaya wuri, yayin da rahotannin farko daga asibitin suka ce wata tartsatsin wuta ta haifar da gobarar da ta bazu cikin sauri saboda iskar oxygen da ake amfani da ita wajen kula da jariran.
Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, ya dakatar da Sakataren Lafiya na tarayya, Aslam Ghauri, daga aiki, tare da bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Ya kuma nuna matuƙar bakin ciki kan mutuwar jariran.
Wasu daga cikin iyalan jariran sun yi zargin cewa kofofin sashen sun kulle, lamarin da ya hana mutane shiga cikin sauƙi domin ceto jariran.































