An sanar da kuɗin kujerar aikin Hajjin 2027 a Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar Alhazai ta Najeriya, NAHCON, ta sanar da kuɗin aikin Hajjin 2027 da maniyyatan Najeriya za su biya.
Farashin ya bambanta gwargwadon yankin da za a tashi zuwa Saudiyya.
A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce gwamnatin tarayya ta amince da kuɗaɗen ne bayan tattaunawa da shugabannin hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi da kuma masu ruwa da tsaki a Saudiyya.
NAHCON ta kuma sanya ranar 26 ga Satumba 2026 a matsayin ranar ƙarshe kuma ta kammala ɗora bayanan na dukkan maniyyatan Hajjin 2027.
Hukumar ta ce ba za a ƙara wa'adin ba.


























