Iran ta ce ta kai hari kan sojojin Amurka a Jordan

Asalin hoton, Getty Images
Iran ta ce ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa kan sansanonin sojin Amurka biyu da ke Jordan, bayan Amurka ta kai hari kan wasu wuraren harba makamai na Iran a tsibirin Larak.
Iran ta ce harin na Amurka ya kashe tare da jikkata sojoji da fararen hula, kuma ta yi alƙawarin ramuwar gayya.
Jordan ta ce ta kakkaɓo makamai masu linzami takwas da suka shiga sararin samaniyarta da sanyin safiyar Litinin.
A halin da ake ciki, farashin ɗanyen mai ya ƙaru da sama da kashi 2%, inda farashin Brent ya haura dala 90 kan kowace ganga.















