Man City na yi wa Maresca maraba a karo na uku a ƙungiyar, Manchester City
Sanarwa daga Manchester City ta jaddada rawar da Enzo Maresca da ya taka wajen taimakawa ƙungiyar ta lashe kofin zakarun Turai da Premier League da FA Cup a 2023.
Shi ne mataimakin Pep Guardiola a wannan kakar a cikin abin da ya kasance karo na biyu daga dan kasar Italiya a Etihad:
"Maresca ya koma City a karo na uku kenan, bayan 2020, inda ya jagoranci karamar kungiyar City zuwa gasar Premier 2 a kakarsa ta farko.
"Kungiyarsa ta yi nasara sosai, inda ta kammala da maki 14 a saman tebur - ta yi nasara 17, ta yi nasara biyar da rashin nasara biyu kawai.
"Bayan da ya koma Italiya tare da Parma, ya sake komawa Etihad a 2022 a matsayin daya daga cikin mataimakan, Pep Guardiola, ya kuma taka muhimmiyar rawa a cikin ma'aikatan, wanda ya taimaka wa kungiyar da ta samu nasarar da ba ta taba yi ba a tarihinta na shekara 132 da lashe manyan kofi uku rigis a kaka daya.
"An nada Maresca a matsayin babban koci a Leicester City, wanda ya kai ta Premier League daga Championship a kakarsa ta farko a kungiyar.
"Ya jagoranci Chelsea zuwa lashe Uefa Conference League kuma ya sami cancantar shiga gasar zakarun Turai ta Uefa a kamfen dinsa na farko a Stamford Bridge, kafin ya jagoranci su zuwa gasar cin kofin duniya ta FIFA wato Fifa Club World Cup da a aka yi a Amurka.


