Dan wasan tawagar Senegal, Pape Gueye, ya ce zai "ɗauki hutu" daga buga wa ƙasarsa wasanni muddin masu horarwar na yanzu suna kan aiki.
Matashin mai shekaru 27 ya yanke wannan shawara ne bayan da Senegal, wadda Pape Thiaw ke horarwa, ta bari aka farke kwallo biyn da ta fara ci 2-0, kafin daga baya Belgium ta farke ta kuma kara na uku daf a tashi a bugun fenariti da ta kai an fitar da ita a zagaye na ƴan 32 a gasar cin kofin duniya ranar Laraba.
Habib Diarra da Ismaila Sarr suka fara ci wa Senegal kwallayen, amma kuma Belgium ta farke a zagaye na biyu ta hannnun Romelu Lukaku da Youri Tielemans.
An bai wa Belgium fenariti mai cike da cece-kuce a minti na 125, kuma Tielemans buga ya ci, abin da ya sa Senegal ta fita daga gasar kenan.
Gueye, wanda ke taka leda a ƙungiyar Villarreal a gasar La Liga a Sifaniya da shi aka fara wasan na Belgium daga baya aka sauya shi da Lamine Camara bayan minti 66.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Gueye, wanda ya buga wa Senegal wasa 45 tare da zura ƙwallaye biyu a nasarar da suka samu kan Iraki a matakin rukuni, ya ce:
"Zan dawo nan gaba in yi wasu bayanai game da dalilin ficewarmu daga gasar... amma a yau ina sanar da cewa muddin waɗan nan masu horarwa ne a kan aiki, zan ɗauki hutu daga buga wa tawagar ƙasar wasanni."
Pape Thiaw yana jagorantar Senegal tun daga watan Disambar 2024, wanda ya jawo dalilin da aka karbe kofin nahiyar Afirka Afcon da Senegal a 2025 a Morocco.
A wasan ƙarshe a AFCON a watan Janairu, Thiaw ya umarci ƴan wasansa su fice daga fili bayan an bai wa Morocco fenariti a lokacin da ake daf da tashi a wasan.
Daga bisani suka dawo filin bayan jinkiri na kusan minti 17, Morocco ta buga fenaritin, amma aka tare kwallon da Brahim Diaz ya buga, sannan Gueye ya ci ƙwallar da ta kai Senegal ta lahe kofin.
Sai dai a watan Maris, Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta ayyana Morocco a matsayin zakarun gasar bayan da ta soke sakamakon wasan ƙarshe dalilin ficewar da Senegal ta yi daga fili yayin wasan.