Foden ya tsawaita kwantaraginsa a Man City
Dan wasan Manchester City Phil Foden ya sabunta kwantaraginsa a ƙungiyar na tsawon shekara huɗu zao ci gaba da zama a ƙungiyar har zuwa 2030.
Poden mai shekara 26 kwantaraginsa za ta ƙare ne a kaka mai zuwa, amma ya amince ya tsawaita ta ya yi aiki tare da sabon kocin ƙungiyar Enzo Maresca.
Dan wasan ya fara bugawa babbar tawagar Manchester City lokacin yana ɗan shekara 17 ƙarƙashin tsohon kocin ƙungiyar Pep Guardiola, daga nan ya buga wa City wasa 369 ya ci Premier shida da Champion Lig ɗaya da kuma FA biyu.
Kocin Ingila da ya jagorance ta zuwa kofin duniya Thomas Tuchel bai tafi da shi gasar ba, saboda rashin ƙoƙarinsa a kakar da aka ƙare, wadda ya fara wasa 23 a cikinta.
Forden ya ce "ya ƙagu ya fara wasa" ƙarƙashin Maresca wanda ya yi aiki tare da tsohon kocin ƙungiyar Guardiola.