Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya a sauran sassan duniya, Juma'a 28/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya a sauran sassan duniya, Juma'a 28/08/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Amurka ta sanya takunkumi kan Bankin Misra a Hadaddiyar Daular Larabawa

    Amurka ta ɗauki matakin sanya takunkumi kan ɗaya daga cikin manyan bankunan Masar, Banque Misr, a Hadaddiyar Daular Larabawa, a wani sabon mataki na ƙara matsin tattalin arziki kan Iran.

    Ma’aikatar Baitulmalin Amurka ta ce tana shirin hana rassan bankin na UAE damar yin mu’amala kai tsaye da cibiyoyin kuɗi na Amurka, musamman harkokin da suka shafi dalar Amurka, saboda zargin alaka da mu’amalolin kuɗi da Iran.

    Matakin ya shafi rassan Banque Misr guda shida da ke UAE, kuma an fitar da shi ne domin a bai wa jama’a damar bayyana ra’ayoyinsu na tsawon kwanaki 30 kafin a fara aiwatar da shi a hukumance.

  2. Jagoran addinin Iran ya haramta kalaman rashin nuna kishin ƙasa

    Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Mojtaba Khamenei, ya bayyana goyon bayansa ga gwamnatin Shugaba Massoud Pezeshkian, tare da yin kira da a guji kalaman da za su iya karya ƙwarin gwiwar jama’a ko rashin kishin ƙasa.

    A wani saƙo da kafafen yaɗa labaran Iran suka fitar a ranar Juma’a daga Khamenei, ya ce duk wani abu da zai iya kawo illa ga haɗin kan al’umma bai kamata a yi shi ba.

    Ya ce kalaman da za su raunana gwiwar al’umma, da kuma ƙirƙirar rarrabuwar kawuna, kamar batun yaƙi ko tattaunawa, haɗin kai ko tsattsauran ra’ayi, da sasantawa ko yaƙi, sun haifar da illa ga al’ummar Iran a baya, kuma hakan na iya sake faruwa.

    “Ina bayyana cewa yin duk wani abu da zai cutar da haɗin kan al’umma haramun ne,” in ji shi.

    Khamenei ya kuma yi kira da a maida hankali kan abin da Iran ta kira “tattalin arzikinta”, tare da rage dogaro da dalar Amurka.

    Ya ce ya kamata a ƙara maida hankali kan bunƙasar tattalin arziki, zuba jari da karkatar da shi zuwa abubuwan da suka fi amfani al'umma da bunƙasa samar da kayayyaki a cikin gida.

    Tun daga ranar 29 ga watan Maris ba a sake ganin Mojtaba Khamenei a bainar jama’a ba, bayan da aka kai hari kan gidan mahaifinsa, Ali Khamenei, wanda shi ne tsohon jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran, a wani hari da Amurka da Isra’ila suka kai.

    Haka kuma ba a fitar da wani hotonsa ba ko a lokacin jana’izar mahaifinsa.

    Wannan ya haifar da raɗe-raɗin da ke nuna shakku kan lafiyarsa, har ma da batun ko yana raye.

  3. Amurka ta wallafa sabbin sunayen ƴan Najeriya 10 da za ta kora saboda aikata laifuka

    Hukumar Shige da Fice ta Amurka, ICE, ta fitar da sabbin sunayen ƴan Najeriya 10 da take shirin kora daga ƙasar bisa zargin aikata laifuka.

    An wallafa sunayen mutanen ne a shafin ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurka, DHS, mai taken “Worst of the Worst”, wato “mafi muni cikin masu laifi”.

    Laifukan da aka lissafa sun haɗa da zamba da satar bayanai, laifukan da suka shafi cin zarafinn yara, laifukan miyagun ƙwayoyi da kuma mallakar makamai.

    Ga sunayen mutanen 10 da laifukan da aka danganta da su:

    • Temitope Bashua — zamba da satar bayanai
    • Ojehoro Lewis — cin zarafin yaro
    • Osemudiamen Kingsley Oziegbe — zamba ta intanet
    • Daniel Oworen — laifin miyagun ƙwayoyi
    • Raymond H. Ekevwo — zamba ta intaneta
    • Franklin Dikeocha — laifin lalata da yaro, ciki har da shafa masa jiki da niyyar lalata
    • Johnson Ogunlana — zamba da satar bayanai
    • Chukwuemeka Okorocha — zamba ta intanet, laifin miyagun ƙwayoyi, mallakar makami da kai wani mummunan hari
    • Tunde Korede — haɗa baki wajen aikata laifi
    • Chukwuemeka Chinye — sata daga cibiyar hada-hadar kuɗi, zamba, fashi, satar bayanai

    Bayanan da aka wallafa a shafin na DHS, an bayyana su a matsayin baƙin haure da ICE ta kama bisa laifukan da ake zarginsu.

    Ma’aikatar ta ce ƙarƙashin jagorancin DHS, jami’an ma’aikatar da ICE suna aiwatar da alƙawarin Shugaba Donald Trump na korar ɗimbin baƙin haure daga Amurka, inda suka fara da waɗanda ta bayyana a matsayin masu aikata manyan laifuka.

  4. Ƴan Najeriya sama da 10,000 suka kamu da cutar mashaƙo a 2026 – NCDC

    Cibiyar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka ta Najeriya (NCDC) sama da mutane 10,000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar mashaƙo a 2026.

    Darakta-Janar na NCDC, Dakta Jide Idris, ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a wani taron manema labarai kan halin da ake ciki game da barkewar cutar kwalara da mashaƙo a Najeriya.

    Ya ce duk da cewa adadin na da yawa, yawan mutanen da suka mutu daga cikin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar ya ragu sosai idan aka kwatanta da makamancin lokacin bara.

    Sai dai Dakta Idris ya ce an samu raguwar masu kamuwa da cutar kwalara a farkon shekarar nan, idan aka kwatanata da 2025.

    Dakta Idris ya ce an samu rahoton sama da mutum 65,000 da ake zargin sun kamu da kwalara a jihohi 35 da kuma kusan ƙananan hukumomi 195 a bana, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    "Adadin mutanen da suka mutu cikin waɗanda aka ruwaito sun kamu da cutar ya ragu sosai idan aka kwatanta da irin wannan lokaci a bara," in ji shi, inda ya yi gargadin cewa har yanzu ana samun yaɗuwar cutar a sassan ƙasar.

    Dakta Idris ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen ɗaukar matakan dakile barkewar cututtukan.

    Ya kuma yi kira ga iyaye da su tabbatar an yi wa yaransu cikakken allurar rigakafin cutar mashaƙo.

  5. XI Jingping ya yi taron gaggawa kan aikin ceto a Tibet da Nepal

    Shugaban China, Xi Jinping ya gudanar da wani taron gaggawa domin tattauna yadda za a ci gaba da aikin ceto, bayan mummunar ambaliya da zaftarewar ƙasar da suka faru a ranar Laraba a iyakar Tibet da Nepal.

    Ƙasar China ta kuma yi tayin ba da tallafin agaji ga Nepal, inda sama da mutum 500 suka mutu sakamakon bala’in.

    Firayim Ministan Nepal ya ce an tura ƙarin ɗaruruwan sojoji domin taimakawa wajen gano da kuma kwaso gawarwakin mutanen da suka mutu.

    Gwamnatin ƙasar ta ce hanyoyin sadarwa da na sufuri sun yanke ga yankunan da bala’in ya fi shafa.

    Yayin da ake ci gaba da aikin bincike da ceton, iyalai da dama na zaman jiran labari kan halin da ‘yan’uwansu ke ciki.

    Ma’aikatan agaji sun bayyana lamarin a matsayin mummunan tashin hankali. Kusan mutum 1,000 ne suka ɓace, kuma fiye da rabinsu masu yawon buɗe ido ne.

    Shugaban Ƙungiyar agaji ta Red Cross (IFRC) a Nepal, David Fisher, ya ce har yanzu akwai fargaba game da yiwuwar sabbin ambaliya da za su iya afkawa ƙasar a nan gaba.

    Da yake magana a wani taron manema labarai a safiyar yau, Fisher ya ce ana hasashen cewa kusan mutum 93,000 ne bala’in ya shafa.

  6. Sudan ta janye dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon shekata biyu a Khartoum

    Gwamnatin Sudan ta sanar da janye dokar takaita zirga zirga da kuma dokar ta-baci da aka shafe shekaru biyu ana aiwatarwa a birnin Khartoum, yayin da take ƙoƙarin mayar da rayuwa yadda take a babban birnin da ya yaƙi ya daidaita.

    Yanzu mazauna birnin za su iya zirga-zirga da gudanar da ayyukansu a kowane lokaci, duk da cewa jami'an tsaro za su ci gaba da sintiri tare da gudanar da bincike.

    Zuwa yanzu mutum fiye da miliyan biyu sun koma Khartoum tun bayan daina yaƘi a birnin.

    Sabbin ƙa'idoji da aka sanya kuma za su hana baƙi shiga Khartoum ba tare da biza ko takardar izini ba.

    Wannan mataki na zuwa ne yayin da cibiyoyin gwamnati ke ci gaba da komawa babban birnin, duk da cewa sojin Sudan da dakarun RSF na ci gaba da gwabza faɗa tsakaninsu a wasu sassan ƙasar.

  7. An sake kama Bello Bodejo jim kaɗan bayan EFCC ta sake shi

    Lauyoyin da ke kare shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore na ƙasa Bello Bodejo sun zargi hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya – DSS - da sake kama shi jim kaɗan bayan sakin sa daga hukumar yaƙi da rashawa ta ƙasar EFCC, ba tare da bayar sanar da su dalili ba.

    A watan Yuli ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, babban birnin ƙasar ta bayar da belin jagoran ƙungiyar bayan shafe kimanin wata hudu a tsare, sai dai lauyoyi da kuma iyalinsa ba su kammala cika ƙa’idojin belin ba har sai cikin makon nan inda aka sake shi a yau Juma’a, bayan zargin shi da laifin halasta kuɗin haram.

    Ɗaya daga cikin lauyoyin da ke kare Bodejo a kotu, Muhammad Sharif ya ce: "EFCC ta sake shi, su kuma DSS sun kama shi a yau. Za mu ƙalubalanci wannan abu da suka yi a kotu, idan suna da hujja game da wannan kamun da suka yi masa sai su gurfanar da shi a kotu."

    Tun farko kotu ta buƙaci Bodejo da ya tanadi naira biliyan biyu a, da mutumin da zai tsaya masa, wanda ya mallaki kadarar da ta kai darajar naira biliyan biyu da kuma takardun biyan haraji na shekara uku.

    Sai dai daga baya kotu ta sassauta ƙa’idojin belin, inda aka buƙaci Bodejo ya tanadi naira biliyan ɗaya a matsayin kuɗin beli da kuma mutane biyu da za su tsaya masa.

    Cikin waɗanda za su tsaya masa wajibi ne ɗaya ya mallaki kadarar da darajarta ta kai naira biliyan ɗaya a unguwar Guzape, ko Asokoro ko kuma Maitama.

    A ranar 9 ga watan Yuli ne hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC ta gurfanar da Bello Bodejo a babbar kotun tarayya da ke Abuja kan tuhume-tuhume shida, waɗanda dukkaninsu ya musa.

    Daga cikin zarge-zargen akwai na karɓar tsabar kuɗi masu alaƙa da gwamnatin jihar Bauchi, waɗanda suka zarce yawan da aka ƙayyade a hukumance.

    Kotun ta ɗaga ranar fara shari’ar zuwa ranakun 5 da 6 da kuma 7 ga watan Oktoban 2026.

  8. Sarkin da ya hau mulki a shekara 3 ya rasu

    Wani sarki a Uganda da aka sani a matsayin mafi ƙarancin shekaru cikin sarakunan duniya ya rasu yana da shekara 34 a duniya, kamar yadda firiministan ƙasar ya sanar.

    Oyo Nyimba Kabamba Iguru Rukidi na IV ya zama Sarkin Tooro a yammacin Uganda yana da shekara uku kacal a shekarar 1995 bayan rasuwar mahaifinsa.

    Masarautar Tooro ba ta bayyana musabbabin rasuwar Sarki Oyo ba, sai dai wani ministan gwamnatin Uganda ya shaida wa kafafen yaɗa labaran cikin gida cewa ya kasance cikin matsanancin rashin lafiya kuma yana neman magani a Amurka.

    Ko da yake Uganda na da shugaba da majalisar dokoki da jama'a ke zaɓa, ƙasar na da masarautun gargajiya da dama waɗanda ke ci gaba da kasancewa masu gagarumar tasiri a fannin al'adu duk da cewa ba su da ikon siyasa.

    Oyo, wanda kundin adana tarihi na Guinness ya ambata a matsayin mafi ƙarancin shekaru cikin sarakunan duniya masu mulki, ya mulki fiye da mutum miliyan biyu a faɗin masarautarsa.

    Shi ne sarki na 13 a Masarautar Tooro, wadda aka kafa a farkon ƙarni na 19.

    Yayin sanar da rasuwarsa, Firimiyan Tooro, Calvin Armstrong Rwomiire Akiiki, ya bayyana mutuwarsa a matsayin "gagarumin rashi da ba za a iya misalta shi ba" ga iyalan sarauta da kuma ilahirin al'ummar Tooro.

    "Ina kira ga ɗaukacin al'ummar Tooro su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai, nutsuwa da kuma addu'a a wannan lokaci mai matuƙar wahala," in ji Akiiki a jawabin da ya yi ranar Juma'a.

    Masarautar Tooro na bin tsarin gado wajen zaɓen sarki, inda sarauta ke wucewa daga iyaye zuwa ƴaƴa ko wasu daga cikin dangin sarauta.

  9. Qatar da Iran sun tattauna kan mashigar Hormuz

    Firaministan Qatar da kuma Ministan Harkokin Wajen ƙasar, Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani, sun kai ziyara Tehran, babban birnin Iran, inda ya gana da shugabannin ƙasar.

    Tattaunawar ta mayar da hankali kan makomar mashigar Hormuz, musamman wani shiri na samar da wata hanya ta wucin gadi da jiragen ruwa za su riƙa amfani da ita.

    Haka kuma sun tattauna kan wani shiri na haɗin gwiwa domin cire nakiyoyin ruwa da aka ce an dasa a mashigar a lokacin yaƙi.

    Ɓangarorin biyu sun kuma tattauna hanyoyin rage tashin hankali a yankin da samar da yanayin da ya dace don sake fara tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

    Sheikh Mohammed ya kuma gana da Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, da Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, wanda kuma shi ne babban mai shiga tsakani na Iran a tattaunawa.

  10. Dokar tsaurara sauya addini ta fara aiki a jiha ta 13 a Indiya

    Wata sabuwar doka da za ta riƙa lura da al'amuran addini ta fara aiki a jihar Maharashtra ta ƙasar Indiya.

    Jihar wadda ke ƙarƙashin jagorancin jam'iyyar masu kishin addinin Hindu ta Firaiminista Narendra Modi, wato BJP, ta ce dokar ta haramta abubuwa ne da suka shafi tilasta sauya addini, ko yaudara lokacin aure.

    A yanzu za a buƙaci duk wanda zai sauya addini ya cike takardar neman yin hakan a hukumance, watanni biyu gabanin lokacin sauya addinin.

    Duk wanda zai jagoranci sauya wa wani addini dole sai ya tabbatar cewa an bi doka.

    Maharashtra ta zama jiha ta 13 da ta amince da irin wannan doka a shekarun baya-bayan nan - inda mafi yawan jihohin da suka rungumi dokar ke ƙarƙashin jagorancin jam'iyyar BJP.

    Yanzu haka akwai ƙararraki da dama a kotu waɗanda ke ƙalubalantar halascin dokar, inda ake zargin cewa ta saɓa wa ƴancin da kundin tsarin mulkin ƙasar ya bai wa al'umma.

  11. Za mu iya yin aiki da Peter Obi da Kwankwaso don ceto Najeriya - Atiku

    Dantakarar shugaban Najeriya na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar ya ce zai iya yin aiki da sauran jiga-jigan adawar ƙasar domin ceton ƙasar a 2027.

    Masu lura da al'amuran siyasa da dama a kadsar na ganin cewa rabuwar kawunan ƴan hamayyar zai iya raunana yunƙurinsu na kawar da Tinubu a zaɓen 2027.

    To sai dai a hirarsa da BBC, Atiku Abubakar ya ce haɗewar tasu gabanin zaɓen ba abin mamaki ba ne.

    ''Za ku iya wayar gari ku ji labarin mun haɗe, mu yi aiki tare domin ceto Najeriya da talakawan ƙasar'', kamar yadda ya bayyana.

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce babu abin da zai gagara a wannan ƙudiri idan Allah ya nufa.

  12. Abu 4 da gwamnatin Tinubu ta ce ta yi da kuɗin tallafin man fetur da ta tara

    Gwamnatin Najeriya ta bayyana adadin kuɗaɗen da ta fara daga tallafin man fetur da ta cire a watan Mayun 2023.

    A lokacin cire tallafin, Shugaba Tinubu ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon yadda ake zargin cewa wasu tsiraru na amfani da tallafin wajen arzurta kansu.

    Inda kuma ya ce za a yi amfani da kuɗin wajen gudanar da ayyukan cin gaban ƙasa.

    Sai dai tun bayan cire tallafin ƴanƙasar da dama sun ci gaba da aza ayar tambaya kan nawa gwamnatin ta tara, kuma me ta yi da shi.

    To amma a karon farko gwamnatin ta bayyana kuɗaɗen da ta tara sakamakon matakin da yadda ta kashe su.

  13. 'Amurka ta nemi Rasha ta hana Iran bayanan sirri'

    Majiyoyi masu tushe sun shaida wa kafafen yaɗa labaran Amurka cewa daraktan Hukumar Leken Asirin Amurka (CIA), John Ratcliffe, ya roƙi jami’an leken asirin Rasha kada su bai wa Tehran bayanan da za su iya amfanarta.

    Bayanai sun ce yayin wata ziyarar sirri da ya kai Moscow, batun goyon bayan da Rasha ke bai wa Iran na daga cikin muhimman abubuwan da aka tattauna.

    Wannan ita ce ziyara ta farko da aka bayyana a fili da wani shugaban CIA ya kai Moscow tun shekarar 2021.

    Fadar Kremlin ta tabbatar da cewa Mista Ratcliffe ya gana da jami’an leken asirin Rasha, amma ba da Shugaba Putin ba.

    Baya ga batun Iran, rahotanni sun ce Ratcliffe ya tattauna da jami’an Rasha kan damuwar Amurka game da tsaron ƙasashen ƙungiyar NATO.

    Sai dai jami’an Amurka da na Rasha ba su fitar da cikakkun bayanai a hukumance kan abin da aka tattauna ba, yayin da CIA ta ƙi yin tsokaci kan ziyarar.

    Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana ziyarar a matsayin irin ta yau da kullum, yana mai cewa irin waɗannan tattaunawa na iya taimakawa wajen ciyar da wasu batutuwa gaba, ciki har da kawo ƙarshen yaƙin Ukraine.

    Sai dai bai bayar da cikakken bayani kan tattaunawar da aka yi da Rasha ba.

    A cikin watannin baya-bayan nan, an sha samun rahotannin da ke magana kan taimakon da hukumomin leƙen asiri na China da Rasha suka bai wa Iran a lokacin yaƙinta da Amurka da Isra’ila.

    A nata ɓangaren, Moscow ta sha zargin Washington da ƙawayenta na Turai da bai wa Ukraine taimakon leƙen asiri, tare da yin kira ga Amurka ta dakatar da irin wannan taimako.

  14. An naɗa sabon sarkin Norway bayan rasuwar sarki Harald IV

    Sarki Haakon na Takwas ya hau karagar mulkin Norway bayan rasuwar mahaifinsa, Harald na Biyar.

    Taron jama'a masu yawa ne suka fito domin shaida isowar sabon sarkin a Fadar masarautar da ke birnin Oslo, inda yake ganawa da ministocin gwamnati.

    Sarki Harald ya rasu ne a safiyar yau Juma'a yana da shekaru 89 a duniya.

    Ya kasance sarki mai farin jini, inda ya shafe sama da shekaru 30 yana mulki.

    Ana yaba masa da kawo sauye-sauye da zamanantar da masarautar Norway.

    Haka kuma ya karya wata tsohuwar al'ada ta sarauta lokacin da ya auri gimbiya Sonja, wadda ba ta fito daga gidan sarauta ba.

    Gwamnatin Norway ta ayyana makoki a faɗin ƙasar domin alhinin rasuwar sarkin.

  15. Ya kamata a kyautata rayuwar talaka bayan cire tallafin mai - Atiku

    Kusan mako biyu ke nan ana ta ce-ce-ku-ce tun bayan da tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana aniyarsa ta cire tallafin man fetur idan ya hau kan mulki a 2027.

    Kamar mutane da dama a Najeriya, Atiku na ganin cewa cire tallafin man fetur shi ne silar matsalolin matsin tattalin arziƙi da al'ummar ƙasar ke ciki.

    "Ana cikin ƙunci, ana cikin rashi da rashin aikin yi, wannan tallafin man fetur da aka janye shi ne babban abin da ya haifar da hakan. Ban taɓa ganin an sha wahala ba a ƙasar nan kamar wannan lokaci," in ji Atiku a tattaunawar da BBC.

    Gwamnatin Najeriya ta mayar wa Atiku martani, inda ta bayyana cewa batun tamkar rashin fahimtar abin da ke faruwa ne da tattalin arziƙin ƙasar.

    Sai dai a tattaunawar da BBC, Atiku ya ce cire tallafin man fetur da zai yi ya dogara ne da halin da ya tsinci ƙasar idan ya kama mulki.

    Atiku ya ce: "Ko za ka cire tallafin man fetur, ba a lokaci ɗaya za ka yi shi ba , kuma sai ka kyautata rayuwar talakawa kafin ka fara cirewa a hankali".

    A ranar 29 ga watan Mayun 2023 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a ƙasar.

    Lamarin ya haifar da tashin farashin man fetur nan take, wani abu da ya shafi dukkanin fannonin rayuwa na al'ummar ƙasar.

    Haka nan Najeriya na fama da tashin farashin kayan masarufi, wanda duk ake alaƙantawa da cire tallafin na man fetur.

    Tun farko gwamnatin Tinubu ta yi alƙawarin samar da shirye-shirye da za su sauƙaƙa wa al'ummar ƙasar tsananin rayuwa, to amma sama da shekara uku bayan cire tallafin al'umma da dama a ƙasar na cewa ba su ga wannan tallafi ba.

    Ministan Kuɗin Najeriya, Taiwo Oyedele ya ce an tara jimillar naira tiriliyan 15.8 daga kuɗaɗen tallafin man fetur ɗin tsakanin watan Yunin 2023 da Disamban 2025.

    Ministan ya ce gwamnatin ta kashe kuɗaden ne ta hanyar raba wa jihohi da yin ƙarin albashi da alwus ɗin ma'aikata da biyan basukan da ake bin ƙasar da kuma gudanar da manyan ayyuka.

  16. 'Amurka na yunƙurin mallakar wani kaso na man Venezuela'

    Rahotannin daga kafafen yaɗa labaran Amurka sun ce gwamnatin shugaba Donald Trump na tattaunawa da gwamnatin riƙon ƙwaryar Venezuela kan yiwuwar Washington ta mallaki wani kaso na ɗimbin arzikin man fetur ɗin ƙasar.

    Rahotannin sun ce tattaunawar ta shafi fiye da filayen hako man fetur 12 masu samar da mai, waɗanda ke ɗauke da ganga biliyan 90 na ɗanyen mai, wato kusan kashi ɗaya bisa uku na man da Venezuela ke da shi.

    Kamfanin dillancin labarai na Axios( Acius) ya ce, a ƙarƙashin shirin, kamfanoni masu zaman kansu ciki har da na Amurka za su bunƙasa waɗannan filayen mai, yayin da Venezuela kuma za ta ƙara samun kuɗaɗen shiga daga man.

  17. Tun da na zama gwamnan Kaduna ban karɓi bashin kobo ba - Uba Sani

    Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce gwamnatinsa ba ta karɓi wani sabon bashi ba tun bayan da ya hau mulki a 2023, duk da cewa tana ci gaba da biyan bashin da ta gada daga gwamnatocin baya.

    Uba Sani ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na tashar talabijin ta Channels TV a ranar Alhamis, yayin da yake amsa tambayoyi kan yadda gwamnatinsa ke kashe kuɗaɗe da kuma ƙarin kuɗaɗen shiga da jihar ke samu.

    A cewar gwamnan, a halin yanzu Jihar Kaduna tana ware kimanin naira biliyan 6.7 a kowane wata domin biyan bashin da ta gada daga gwamnatocin da suka gabata.

    “Tun da na zama gwamna, ban karɓi koda kwabo ɗaya na bashi ba,” in ji gwamnan.

    Ya danganta wannan mataki da abin da ya bayyana a matsayin tsantsar kula da harkokin kuɗi cikin hikima da kuma yin taka-tsantsan wajen tsara abubuwan da gwamnati za ta kashe kuɗinta a kansu.

    “Batu ne na yin taka-tsantsan da yin abin da ya kamata, da kuma ta zaɓar wuraren da suka dace a zuba jari cikin kulawa sosai,” in ji shi.

    Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa gwamnatinsa ta samu nasarori masu yawa, yana mai nuni da ci gaban da aka samu a fannonin noma da ilimi da bunƙasa sana’o’i da kuma tsaro.

    Jihar Kaduna dai na daga cikin jihohin arewacin ƙasar da ke fuskantar matsalolin tsaro, musamman yanbindiga masu garkuwa da mutane.

  18. 'Da mun shirya kai wa Trump hari a Turkiyya ba abin da zai hana mu aiwatarwa'

    Sakataren Majalisar Tsaron Iran, Mohsen Rezaei ya ce Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ne ya kitsa cewa Iran ta yi yunƙurin kashe Trump domin ƙara harzuka shi ya ci gaba da yaƙi da Iran.

    Cikin wata hira da kafar yaɗa labarai ta Al-Manar mai watsa shirye-shirye da harshen Larabci, mai alaƙa da ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon, Mista Rezaei ya ce zarge-zargen da ke cewa Iran ta yi yunƙurin "kashe" Donald Trump a lokacin ziyararsa zuwa Turkiyya, tare da "barazanar" kashe ƙaramin ɗansa, wata makarkashiya ce daga Isra'ila.

    Ya ce Benjamin Netanyahu, ne ya ƙirƙiro wannan shiri domin ya tsoratar da kuma hgarzuƙa shugaba Trump da nufin Amurka ta ci gaba da yaƙi da Iran.

    A cikin bidiyon hirar, wadda kafafafen yaɗa labaran Iran ciki har da kamfanin dillancin labarai na ISNA suka wallafa wasu ɓangarorinta, Rezaei ya ce “Netanyahu ya tsorata Trump ta hanyar yaɗa labaran ƙarya game da wata maƙarkashiyar da Iran ke yi domin kashe shi, lamarin da ya rikita masa tunani kan matakan da zai ɗauka.

    ''Waɗannan bayanai sun razana Trump, inda ya kiɗime har ya koma kamar mai sayar da abinci a motar raba abincin jirage (a yayin bulaguronsa daga Turkiyya).

    Sakataren tsaron ya ce ko kusa ko alama Iran ba ta ƙudiri wannan aniya ba.

    ''In da mun yanke shawarar yin hakan, babu abin da zai hana mu aiwatar da shi. Amma wannan labarin ba komai ba ne illa dabarar yaudara ta Netanyahu.”

  19. Adadin waɗanda suka mutu a ambaliyar Nepal ya kusan 500

    Mahukuntan ƙasar China sun ce masu aikin ceto sun kwashe fiye da mutum 1,000 daga yankunan da ambaliyar ruwa da zaftarewar ƙasa suka shafa a kudancin yankin Tibet, bayan mummunar ambaliya da zaftarewar ƙasar da ta afku a ranar Laraba.

    Kafar talabijin ɗin China, ta ce fiye da masu yawon buɗe ido 500 na daga cikin waɗanda aka ceto.

    A arewacin Nepal kuwa, ana ci gaba da neman waɗanda suka tsira cikin dare, yayin da ake ci gaba da fargabar aukuwar wata sabuwar ambaliyar.

    An tabbatar da mutuwar kusan mutum 500 a Nepal, amma har yanzu fiye da mutum 800 ba a san inda suke ba.

    Adadin waɗanda suka mutu da jikkata na ci gaba da ƙaruwa a mummunan bala'in da Nepal ta fuskanta tun bayan girgizar ƙasar da ta afku a shekarar 2015.

    Fiye da rabin waɗannan mutanen dai baƙi ne masu yawon buɗe ido da kuma wadanda suka je ibada.

  20. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a, hajji babbar rana, kamar yadda Hausawa ke yi mata kirari.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniyar ke ciki.

    Ku ci gaba da tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta da muharawa.