Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftan ƙasashe da kuma sauran sassan duniya na ranar Asabar 21 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. ICPC ta sake bankado wata hukumar bogi a Najeriya

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan wata sabuwar hukumar gwamnati da ake zargin ta bogi ce, wadda hukumar yaƙi da cin hanci ta ƙasar ta gano.

    Wannan lamari ya biyo bayan wani makamancin bincike da ya shafi wata hukuma da gwamnati ta ce an gabatar da ita a matsayin hukumar gwamnati, alhali ba haka ba ne.

    Hukumar ICPC ta ce hukumar ta National Brands Development and Made in Nigeria Special Project Office tana gudanar da ayyukanta ba bisa ƙa’ida ba daga wani ofishin gwamnati da ke Abuja.

    Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu, ya ce an ware wa hukumar wannan ofishin ne a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ba tare da amincewar Shugaban Ƙasa ba.

    Ya bayyana cewa an gano hakan ne yayin wani babban bincike da Shugaba Tinubu ya bayar da umarni a gudanar, bayan wani rahoto na baya da ya shafi Presidential Foreign Intervention Promotion Council, wadda ake zargin ƙungiya ce da ba ta wanzu a zahiri.

    A cewar Aliyu, wani mutum mai suna George Buchi Nwabueze ne ya ke tallata sabuwar hukumar, kuma ana zargin yana amfani da sunaye daban-daban.

    ICPC ta ce tana binciken yadda aka ba wannan ofishi damar gudanar da ayyukansa daga harabar gwamnati, da kuma ko wasu jami’an gwamnati sun taimaka wajen ba shi damar yin hakan.

    Har yanzu ba a bayyana ko Nwabueze ya samu kuɗi daga wannan zargin ba kafin a gano lamarin.

    A cewar ICPC, Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin a kama Nwabueze ba tare da bata lokaci ba.

    Shugaban ƙasar ya kuma bayar da umarnin dakatar da wasu manyan jami’an gwamnati da ake zargi suna da alaka da hukumar, in ji Aliyu.

    A baya dai wani bincike daban da aka gudanar kan Presidential Foreign Intervention Promotion Council, wadda fadar shugaban ƙasa ta ce ba ta bogi ce.an hukumomin da ake zargin na bogi ne.

  2. Sakataren sojin kasan Amurka zai yi murabus

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga Mujallar Wall Street cewa ana sa ran Sakataren Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka, Dan Driscoll, zai yi murabus kafin ƙarshen shekara, bayan watanni ana samun takun-saka tsakaninsa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth.

    Mujallar Wall Street Journal ta wallafa rahoton ne bisa bayanan wasu mutane da ke da masaniya kan dambarwar.

    Sai dai Reuters ta ce har yanzu ba ta samu damar tabbatar da rahoton da kanta ba.

    Idan aka tabbatar da murabus ɗin Driscoll, hakan zai sa Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka ta kasance ba tare da shugaba da Majalisar Dattijan Amurka ta tabbatar da nadinsa ba, a daidai lokacin da Washington ke ci gaba da yaƙi da ta ƙaddamar tare da Isra’ila kan Iran, wanda yanzu ya shafe kusan wata shida.

  3. APC ta nada Abdulaziz Yari Darakta-Janar na yakin zaben Tinubu

    Jam’iyyar APC ta kafa Kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa, inda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya kasance Darakta Janar (DG) na kwamitin.

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima za su kasance shugaba da mataimakin shugaban kwamitin, sannan Gwamna Hope Uzodimma kuma zai yi aiki a matsayin sakataren kwamitin.

    A cikin tsarin kwamitin, an haɗa manyan jami’an jam’iyyar da gwamnati domin jagorantar shirye-shiryen yaƙin neman zaɓen da ake tunkarar zaɓen Janairu 2027.

    Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin da su yi aiki tukuru domin ganin APC ta samu nasara a zaɓen.

  4. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.