KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 24/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftanta da kuma sassan duniya na ranar Litinin 24 ga watan Agusta, 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Bola Tinubu
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello, Haruna Kakangi

  1. An yanke wa babban malamin Musulunci hukuncin ɗaurin rai da rai

    Ahmed al-Sharaa

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaban Syria Ahmed al-Sharaa

    Wata kotu a Syria ta yanke wa wani babban malamin addinin Musulunci hukuncin ɗaurin rai da rai bayan samun shi da laifin tayar da rikici da kuma amfani da muƙami ta hanyar da ba ta dace ba.

    A ƙarƙashin tsohon shugaban ƙasar Bashar al-Assad, Ahmad Hassoun na daga cikin malaman Musulunci masu matuƙar tasiri.

    Wasu na masa laƙabi da ‘mai bakin reza’ saboda tsananin goyon bayansa ga gwamnati.

    Shi ne mutum na 10 a cikin manyan mutanen gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Basar al-Assad da aka yanke wa hukunci ƙarƙashin sabuwar gwamnatin da ta kama mulki bayan hamɓarar da Assad a watan Disamban 2024.

  2. Mun cika alƙawuran da muka ɗauka lokacin yaƙin neman zaɓe - Tinubu

    Bola Tinubu

    Asalin hoton, Bayo Onanuga

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa ta cika alƙawuran da ta ɗauka lokacin yaƙin neman zaɓen 2023, kuma ƙasar na gab da fara cin gajiyar matakan da aka ɗauka.

    A cikin sanarwar da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar na sunayen kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasar na 2027, Tinubu ya ce gwamnatinsa ta sanya Najeriya a kan hanyar samun ci gaban tattalin arziki.

    "Babu shakka mun fito daga cikin duhun da muke ciki, kuma yanzu muna gab da girbar amfanin tattalin arzikin da zai amfani dukkan ƴan Najeriya," in ji Shugaba Tinubu.

    Ya ƙara da cewa yayin da ake tunkarar lokacin yaƙin neman zaɓen, gwamnatinsa na da nasarori da dama da za ta bayyana wa ƴan Najeriya.

    Ya ce za su fito da abubuwan da gwamnatinsa ta cimma domin ƙara wa al'umma fata da ƙarfafa musu gwiwa a sassan ƙasar.

    Tinubu ya kuma ce za su yi nasara kan dukkan masu ƙoƙarin mayar da Najeriya baya.

    Shugaban ya buƙaci dukkan mambobin kwamitin su yi aiki tuƙuru domin ganin jam'iyyar ta samu nasara a zaɓen shugaban ƙasa na Janairun 2027.

  3. Yariman Saudiyya zai tattauna da shugaban Faransa

    Yariman Saudiyya mai jiran gado Mohamed Bin Salman da shugaban Faransa Emmanuel Macron

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Yariman Saudiyya mai jiran gado Mohamed Bin Salman da shugaban Faransa Emmanuel Macron

    Rikicin da ke tsakanin Iran da Amurka na daga cikin manyan batutuwan da za su mamaye tattaunawar da shugaban Faransa Emmanuel Macron da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman za su yi a birnin Paris a yau Litinin.

    Baya ga haka, Macron da Bin Salman za su jagoranci taron farko na sabuwar majalisar hadin gwiwar dabarun siyasa da tattalin arziki tsakanin Saudiyya da Faransa.

    Ana kuma sa ran bangarorin biyu za su rattaba hannu kan yarjejeniyoyi a fannonin da suka hada da lafiya da sufuri da makamashi.

  4. Ƴan awaren Mali sun sake sakin sojoji 20

    Azawad Liberation Front (FLA)

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar masu fafutukar ballewa daga arewacin Mali, wato Azawad Liberation Front (FLA), ta sake sakin wasu sojojin Mali 20 da ta yi garkuwa da su, wasu daga cikinsu sun shafe sama da shekaru uku a tsare.

    Ƙungiyar ta ce sakin sojojin ya biyo bayan musayar fursunoni, inda aka saki wasu fararen hula da hukumomin Mali suka tsare a babban birnin ƙasar, Bamako.

    Wani kakakin FLA ya ce wasu daga cikin sojojin da aka saki suna cikin “mummunan yanayi da ya taba jikinsu da tunaninsu”, bayan wasu daga cikinsu sun shafe kusan shekaru biyar a tsare.

    Sai dai rundunar sojin Mali ta musanta bayanin cewa mutanen da aka musanya da sojojin fararen hula ne.

    Wata majiyar tsaro ta ce a maimakon haka, an saki aƙalla mayakan FLA takwas ne.

    Sojojin da aka saki dai an kama su ne a lokuta daban-daban tun bayan barkewar rikicin Mali, ciki har da fadan da aka yi a ƙarshen watan Afrilu da kuma hare-haren haɗin gwiwa da FLA da ƙungiyar JNIM mai alaƙa da al-Qaeda suka kai a farkon watan Yuli.

    Sakin na baya-bayan nan ya zo ne bayan jerin musayar fursunoni da aka gudanar a Mali cikin kwanakin baya.

    A ranar 13 ga Agusta, an saki sama da sojoji 80 da aka tsare tun watan Afrilu, sannan bayan kwana uku aka sake wasu sojoji shida da suka samu raunuka.

  5. Najeriya ta ƙaddamar da yaƙi ta sama kan ƴan fashin daji

    Jirgin yaƙin sojin Najeriya

    Asalin hoton, NAF/FB

    Rundunar sojin sama ta Najeriya (NAF) ta ƙaddamar da wani shirin yaƙi ta sama a jihohin arewa maso yammacin ƙasar kan “ƴan ta’adda da sauran masu aikata laifuka” da suka addabi yankin.

    A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, rundunar ta ce yaƙin wanda ta yi wa laƙabi da ‘Hannun ƙarfe’ zai tallafa wa sojojin da ke kai samame ta ƙasa domin dawo da tsaro a jihohin Zamfara da Katsina da Sokoto da Kebbi da kuma Kaduna, inda sojoji ke aiki ƙarƙashin shirin ‘Operation Fansan Yamma’.

    “Wannan shiri ya tabbatar da ƙoƙarin dakarun saman Najeriya wajen amfani da dabarun yaƙi ta sama da haɗa hannu da sauran hukumomin tsaro wajen daƙile ayyukan ƙungiyoyin miyagu’.

    Haka nan a cikin wani saƙo na daban rundunar sojin Najeriya ta sanar da wani shiri na kawar da ƴan ƙungiyar Lakurawa a jihohin Sokoto da Kebbi.

    A watan Mayu ƙungiyar IS a yankin Sahel ta yi iƙitrarin ɗaukar nauyin wasu hare-hare a jihohin Sokoto da Kebbi.

  6. Wa'adin da Amurka ta ɗiba kafin 'gallaza' wa Iran ya cika

    xxxx

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban hafsoshin tsaron Pakistan, Field Marshal Asim Munir, zai kai ziyara Iran a yau domin kokarin farfado da tattaunawar da ta kakare tsakanin Tehran da Amurka.

    Zai kai ziyarar ne yayin da Amurka ke shirin sanar da karin takunkuman tattalin arziki kan Iran.

    Sakataren Baitulmalin Amurka, Scott Bessent, ya bayyana matakan a matsayin mafiya tsauri da girma da aka taba shirya wa wata kasa abokiyar gabar Amurka.

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi watsi da barazanar, yana mai cewa alama ce ta rashin mafita da Amurka ke ciki.

    Iran tana nan yadda take, ko gezau, kuma tana ci gaba da barzanar kai hari kan duk wani jirgin ruwa da zai bi Mashigar Hormuz wanda ba ta ba shi izini ba.

    Sai dai kuɗin ƙasar ta Iran, wato Rial, ya faɗi zuwa mafi karancin matsayi a tarihinsa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

  7. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin (Monde tushen aiki) a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.