KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran al'amuran da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar 04/09/2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Buhari Fagge

  1. Koriya ta Kudu na shirin tura dakarunta mashigar Hormuz

    h

    Asalin hoton, Getty Images

    Kafofin yaɗa labarai na Koriya ta Kudu sun ruwaito cewa gwamnatin ƙasar na shirye-shiryen tura kayan aiki da sojoji domin tallafawa abin da ake kira “’yancin zirga-zirga a mashigin ruwa na Hormuz”, kuma tana shirin fara wannan aiki kafin ƙarshen shekarar nan.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito a ranar Alhamis 3 ga Satumba cewa rahotannin kafafen yaɗa labaran Koriya ta Kudu, waɗanda suka ambaci majiyoyin gwamnati da na soja, sun bayyana cewa Seoul na ɗaukar matakan doka da suka dace domin samun amincewar majalisar dokoki kan wannan tura sojoji.

    Bisa ga waɗannan rahotanni, gwamnatin ta tantance shirin a taron majalisar ministoci, tana shirin miƙa buƙatar amincewa a hukumance ga majalisar dokoki a cikin wannan wata.

    Yiwuwar tura sojojin Koriya ta Kudu na zuwa ne a daidai lokacin da matsalolin tsaro a mashigin Hormuz da hare-haren da ake kai wa jiragen kasuwanci suka ƙaru a cikin makonnin baya-bayan nan. Haka kuma, wasu ƙasashe da dama suna nazarin hanyoyin da za su shiga cikin ƙoƙarin kare tsaron harkokin sufuri ta ruwa a wannan muhimmin mashigin ruwa.

    Ya zuwa yanzu, jami’an gwamnatin Koriya ta Kudu ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da waɗannan rahotanni.

  2. Mun yi kuka mun kuma yi murna sosai.......

    ,

    Asalin hoton, Handout to BBC Nepali

    Matar ɗaya daga cikin ma’aikatan da aka ceto, Kabir Maharjan, mai suna Hirashova, ta shaida wa BBC Nepali irin farin cikin da take ciki bayan an gano mijinta da rai.

    Ta ce "Na ga hotunansa a Facebook. Na yi matuƙar farin ciki. Yanzu suna kawo shi Asibitin Sojoji da ke Kathmandu. Ni ma ina kan hanyata ta zuwa asibitin."

    Ta ƙara da cewa "Tsawon kwanaki 10 ba mu iya cin abinci ko shan ruwa yadda ya kamata ba. Mun kasance cikin tsananin fargaba. Yanzu kuma dukkanmu muna cikin farin ciki. Har ma muna kuka saboda murna."

    Maganganunta na nuna irin wahala, damuwa da tashin hankalin da iyalansu suka shiga a kwanakin da suka gabata, da kuma babban farin cikin da suka samu bayan da aka ceci Kabir da rai.

  3. Najeriya ta musanta hannu a yunƙurin juyin mulkin Nijar

    ,

    Najeriya ta musanta zarge-zargen cewa ita ko ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka ta Ecowas sun goyi bayan wani yunƙurin juyin mulki da ake zargin an yi a ƙasar Nijar mai maƙwabtaka da ita.

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta bayyana cewa zarge-zargen da ke yawo da su a shafukan sada zumunta “ba su da tushe bare makama, kuma wani yunƙuri ne na yaudarar jama’a da kuma ɓata sunan Najeriya.”

    Sanarwar ta biyo bayan zargin da wani kyaftin ɗin rundunar sojin Nijar ya yi cewa wasu gwamnatocin ƙasashen waje, ciki har da Faransa, Chadi da Côte d’Ivoire, da kuma mutanen da ke da alaƙa da hambararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum, sun shirya tsoma baki cikin wani rikicin da ya faru a wani sansanin soja a birnin Niamey makon da ya gabata.

    Kyaftin Roger Gabriel, kwamandan Bataliya ta Farko ta Sojojin Saman Nijar, ya kuma yi zargin cewa shugaban ƙasar Benin, Patrice Talon, ya samu amincewar Ecowas domin shiga tsakani.

    BBC ta tuntubi gwamnatoci da mutanen da aka ambata a zargin domin neman bayani.

    Faransa ta ƙi cewa komai kai tsaye, amma ta shaida wa BBC cewa duk wani matakin tura sojojinta ƙasashen waje ana yin sa ne tare da haɗin gwiwar ƙasashen abokan hulɗarta.

    Babu dai wanda ya tabbatar da wannan zarge-zargen da Kyaftin Gabriel ya yi, sannan kuma bai gabatar da wata hujja ba a bainar jama’a da za ta tabbatar da ikirarinsa ba.

    Dangantaka tsakanin Najeriya da Nijar ta yi tsami tun bayan da sojoji suka karɓi mulki a watan Yulin 2023 tare da hamɓarar da Mohamed Bazoum.

    A lokacin, Ecowas ƙarƙashin jagorancin shugaban Najeriya na wancan lokaci, Bola Ahmed Tinubu, ta yi barazanar amfani da ƙarfin soja idan gwamnatin mulkin soji ba ta dawo da tsarin mulkin dimokuraɗiyya ba. Hukumomin sojin Nijar sun yi kakkausar suka ga wannan barazana, lamarin da ya ƙara lalata dangantakar ƙasashen biyu.

    Daga baya Ecowas ta ƙaƙaba wa Nijar takunkumi, amma ƙungiyar ta cire su a shekarar 2024. Tun daga wannan lokaci Nijar ta fice daga Ecowas tare da Mali da Burkina Faso, kuma ƙasashen uku masu mulkin soja sun kafa nasu ƙawancen yankin.

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta ce ƙasar ta kasance tana adawa da duk wani canjin gwamnati da ba bisa tsarin mulki ba.

    “Najeriya ba za ta taɓa goyon bayan karya doka ko sauyin gwamnati da ba bisa tsarin mulki ba a ko’ina, komai wanda yake da hannu ko ƙasar da abin ya shafa,” in ji sanarwar.

    Ta ce tuni an fayyace matsayar Najeriya a wata sanarwa da aka fitar a ranar 30 ga Agusta bayan rikicin da ya faru a sansanin soja da ke Niamey.

    “Najeriya na kallon duk wani sauyin gwamnati da ba bisa tsarin mulki ba da matuƙar damuwa. A matsayinta na maƙwabciya mai alaƙar tarihi, ‘yan’uwantaka da al’adu da Nijar, Najeriya ba ta fatan komai sai zaman lafiya, tsaro, dimokuraɗiyya da ci gaba ga Nijar, yankin da kuma Sahel baki ɗaya.”

    Ma’aikatar ta ce Najeriya na ci gaba da jajircewa wajen goyon bayan matsayar Ecowas da Tarayyar Afirka na kin amincewa da karɓar mulki ta hanyar juyin mulki.

  4. Isra'ila ta saki 'yan ƙasar Lebanon biyar

    ,

    Asalin hoton, Getty Images

    Isra’ila ta sanar da cewa za ta saki ‘yan ƙasar Lebanon biyar da ta tsare a kudancin Lebanon.

    A lokaci guda kuma, jami’an Lebanon sun sanar da cewa an miƙa mutum na farko daga cikin rukunin ga rundunar sojin Lebanon.

    Rundunar sojin Lebanon ta bayyana cewa an mayar da ɗaya daga cikin waɗanda ake tsare da su zuwa ƙasar ta hanyar sasancin ta hannun Red Cross.

    Wannan shi ne sakin farko tun bayan tattaunawar watan Agusta tsakanin Beirut da Isra’ila kan sakin wasu fararen hula da aka tsare tun farkon yaƙin Isra’ila da Hezbollah a shekarar 2024.

    Ofishin Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ta cikin wata sanarwa ya ce bayan kammala bincike da tambayoyi, an tabbatar da cewa mutanen fararen hula ne, ba mambobin wata ƙungiya da Isra’ila ke ɗauka a matsayin ta’addanci ba ne, kuma ba su shiga ayyukan ta’addanci ba. Saboda haka, babu wani dalilin ci gaba da tsare su.

    Ofishin Netanyahu ya kuma ce wannan matakin ya biyo bayan wani ƙoƙari da aka yi tsakanin Isra’ila da Lebanon domin gano da kuma dawo da gawarwakin shugabannin al’ummar Yahudawan Lebanon waɗanda aka yi garkuwa da su kuma aka kashe su a shekarun 1980 lokacin yaƙin basasar Lebanon da ya ɗauki shekaru 15.

    Karanta ƙarin labari a nan:

  5. Ma'aikatan sun maƙale ne a cikin bututun na kwanaki tara

    Za mu ci gaba da kawo muku rahotannin kan yadda aikin ceto ke gudana a tashar ruwa ta 3A Hydropower da ke Trishuli.

    Hukumomi sun shaida wa BBC cewa ana sa ran za a ceto kimanin mutane 42 da suka maƙale a wurin.

    ,

    Asalin hoton, NEA

    ,

    Asalin hoton, NEA

  6. Hotonan yadda aka ceto ma'aikatan

    ,

    Asalin hoton, NEA

    ,

    Asalin hoton, Shaktimaya Tamang/BBC Nepali

  7. Da gaske ne ana iya sace wa namiji al'aura?

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Sama da mutum 80 ne aka kashe tsakanin watan Oktoban 2025 zuwa Yulin 2026 kan zargin "satar al'aura," da ake kira shafi-mu-lera, kamar yadda sashen yaƙi da labaran bogi na BBC ya bayyana bayan tattara bayanai daga jami'an ƴansanda a ƙasashe shida na Afirka.

    Kisan na da alaƙa da jita-jitar cewa taɓa kafaɗar mutum kawai zai iya sa al'aurarsa ta ragu ko ta ɓace. Ana ƙara rura wutar matsalar ta hanyar amfani da labaran ƙarya da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta.

    "Sun fara ihu ne cewa mun sace al'aurar wani, kuma ba mu da wata hanyar tsira saboda akwai tarin jama'a," in ji wani makanike ɗan ƙasar Tanzaniya Boniface Mgala, wanda ya shaida wa BBC irin wahalar da ya sha a watan Afrilu lokacin da waɗanda suka yi imanin cewa shi barawon al'aura ne suka yi masa dukan tsiya.

    Abin da ya fuskanta ya yi kama da na bidiyon da BBC ta gani: maza suna cewa al'aurarsu ta ɓace ko sun yi rauni bayan sun haɗu da wasu mutane, sannan akwai taron jama'a suna neman waɗanda ake zargi da aikata laifin su mayar da abin da aka yi zargin sun sace.

    Irin waɗannan ikirari sun samo asali ne daga tsoro da camfe-camfe na baya, musamman a cikin al'ummomin da imani da sihiri ya yi karfi. Kafafen sada zumunta sun ƙara wa waɗannan tsoro.

  8. Manyan ayyuka da gwamnatin Tinubu ke iƙrarin yi a arewacin Najeriya

    Karanta cikakken labarin a nan: https://sauida.shop/hausa/articles/cvgyplrn406o%3C/a%3E%3C/p%3E%3C/div%3E%3C/div%3E%3C/article%3E%3C/li%3E%3Cli class="css-xxlek1">

    Abu 4 da suka hana Najeriya magance matsalar garkuwa da mutane - C.G. Musa

    ..