Har yanzu muna shakkar alaka da Isra'ila - Syria
Ministan Harkokin Wajen Syria ya ce Damascus na sa ran za a sake dawo da tattaunawa da Isra’ila kan yarjejeniyar tsaro nan ba da jimawa ba.
Kwanaki kaɗan bayan da Isra’ila ta kai harin sama kan wani sansanin sojan Syria, Asad Shaibani ya jaddada a wata hira da Reuters cewa babban abin da Damascus ke son cimmawa a yanzu shi ne dakatar da hare-haren Isra’ila.
A cewarsa, domin samun ci gaba a wannan fanni, ya zama dole bangarorin biyu su ɗauki matakai na gina amincewa da juna.
Shaibani ya ce an dakatar da tattaunawar kan yarjejeniyar tsaro tun bayan fara yaƙin Iran, amma yana sa ran za a sake farawa nan ba da jimawa ba. Ya kuma ce an katse hulɗa tsakanin ɓangarorin biyu bayan da Isra’ila ta kai hari kan wani sansanin sojin saman Syria.
Gwamnatin Syria na fatan cimma yarjejeniyar zai kasance mataki na ƙarshe da zai kai ga janye Isra’ila daga yankunan Syria.
Shaibani ya yi kira ga Isra’ila da ta yi amfani da wannan “dama ta tarihi”, yana cewa “ƙofofin diflomasiyya” har yanzu a buɗe suke. Sai dai ya kuma nuna damuwa game da rashin amincewa da juna:
“Mun yi imanin cewa ya kamata a samu hulɗa, musamman da ɓangaren da yake ci gaba da barazana ga tsaron Syria. Amma idan wannan hulɗar ba za ta haifar da wani amfani ba, ba ma buƙatarta. A halin yanzu, ba mu amince da Isra’ila ba.”
Amurka ta kwashe fiye da shekara guda tana ƙoƙarin sasanta tsakanin Isra’ila da gwamnatin Shugaban Syria Ahmed al-Sharaa, wanda Washington ke ɗauka a matsayin sabon abokinta a Gabas ta Tsakiya, domin cimma yarjejeniyar tsaro. Sai dai har yanzu waɗannan ƙoƙarin ba su yi nasara ba.
A wannan lokacin, Isra’ila ta tura dakarunta zuwa cikin yankin Syria tare da kai hare-hare kan wuraren gwamnati da kayan aikin soji, tana mai cewa matsalar tsaro ce dalilin hakan.
Ofishin Firaministan Isra’ila bai mayar da martani ga buƙatar Reuters ta neman bayani kan kalaman ministan na Syria ba.