Kotu za ta yanke hukuncin kan yunkurin korar ƴar Najeriya daga Afirka ta Kudu

Asalin hoton, Getty Images
Ana sa ran cewa wata kotun yankin Cape Town za ta yanke hukunci a yau game da batun Chidinma Adetshina, ƴar Najeriyar da ta lashe sarauniyar kyau a shekarar 2024, bisa yunkurin hukumomi na mayar da ita Najeriya.
A watan Yuni ne aka kama Chidinma bayan ta sake shiga Afirka ta Kudu ta kan iyaka da Mozambique.
Lamarin ya biyo bayan taƙaddama da aka samu game da zaman ta ƴar asalin ƴar Afirka ta Kudu.
An haifi Chidinma ne a ƙasar ta Afirka ta Kudu, inda mahaifiyarta ƴar ƙasar ce yayin da mahaifinta ɗan Najeriya ne.
Sai dai taƙaddama ta kaure game da asalinta bayan da ta cancanci zuwa matakin ƙarshe na zaɓen sarauniyar kyau ta Afirka ta Kudu a shekarar 2024.
Lauyan da ke kare ta na ƙalubalantar tsare ta da aka yi da kuma yunƙurin fitar da ita daga ƙasar yayin da ma'aikatar harkokin cikin gida ta Afirka ta Kudu ta ce ba ta da halastattun takardun ci gaba da zama a ƙasar.






